Sunday, August 23, 2020

A Safiyar Yau Lahadi Rikici Ya Barke Tsakanin Jami'an Tsaro Da 'Yan Kugiyar IPOB 'Yan Kabilar Igbo A Emene, Ta Enugu

An bayar da rahoton cewa mutane da yawa sun mutu lokacin da wasu mambobin kungiyar IPOB 'yan kabilar Igbo suka yi artabu da 'yan sanda a jihar Enugu ranar Lahadi.

โ€˜Yan sanda sun mamaye wani gini lokacin da mambobin kungiyar IPOB suke wani taro a Emene a Enugu. An bayar da rahoton yin artabu da 'yan kugiyar, lamarin da ya sa 'yan sanda su yi amfani da karfi.

Wannan ya haifar da rikici tsakanin โ€˜yan kungiyar IPOB da jamiโ€™anโ€˜ yan sanda da suka fara harbin da bindiga. An ce nan da nan aka tura wata tawaga daga jamiโ€™an tsaro zuwa wurin da abin ya faru sannan kuma suka sami damar kama da yawa daga cikin โ€˜yan kungiyar IPOB. 

Har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka rasa rayukansu ba, amma wani ganau ya ce โ€œmutane da damaโ€ sun rasa rayukansu a rikicin.

Daniel Ndukwe, kakakin rundunar โ€˜yan sandan jihar Enugu, ba a iya samun damar yin magana dashi ba har zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoton. 

Tashin hankalin na ranar Lahadi shine na baya-bayan nan a tsakanin 'yan sanda da membobin kungiyar IPOB tun lokacin da gwamnatin tarayya ta ayyana kungiyar a matsayin kungiyar ta'adda.

Daruruwan masu fafutukar kafa kasar Biafran da aka kama yayin gangaminsu da makamantan su, a sassa daban-daban na kudu maso gabas yanzu haka suna fuskantar shari'a.

No comments:

Post a Comment

Harin ฦณan Bindiga Na ฦ˜ara Ta'azzara A ฦ˜asar Amurka

Mutane 10 Sun Mutu Sakamakon Harin ฦŠan Bindiga A Walmart Na ฦ˜asar Amurka ฦณan sanda sun ce wani ษ—an bindiga ya harbe mutane da da...