Saturday, August 21, 2021

Matasa Sun Kona Masallaci Kurms


A Jahar Delta Dake Kudu Maso Kudancin Najeriya.


Matasan "Jeddo" da ke Karamar Hukumar Okpe a Jihar Delta sun bi Musulmai masu ibada da kuma Hausa tare da kona wani masallaci kurmus, da sunan yin zanga-zangan nuna rashin amincewarsu da kisan shugaban โ€™yan banga na yankin, mai suna George Akiru wanda aka fi sani da Scosco wanda ba  asan ko suwaye suka kashe shi ba.

Matasan sun zargi Hausawa da cewa sune suka shirya wannan aika-aika ba tare da hujja ba na zargin Hausawa da aikata laifin.

Kisan shugaban 'yan banga ya haifar da tashin hankali a yankin yayin da matasan suka sha alwashin daukar fansar mutuwar mamacin.

Wani matashi a cikin unguwar, Ubada Umukoro, wanda ya zanta da manema labarai ya ce, "Ba da jimawa ba za mu sake kai hari saboda sun kashe dan asalin garin nan."

Mukaddashin jamiโ€™in hulda da jamaโ€™a na rundunar โ€˜yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe, a tattaunawar wayar tarho da DAILY POST, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike don bankado wadanda suka kashe shugabanโ€˜ yan banga.

TARIHIN KUNGIYAR TALIBAN

                 KUNGIYAR TALIBAN

Daga Alkalamin wani bawan Allah

Mulkin Kasar Afghanistan dai a yau ya koma hannun Taliban, sai naga ya dace na warware wasu daya cikin alโ€™ummar mu wani abu mai rikitarwa game da su:

(1) Wannn suna Taliban, a harcen su na Pashtun yana nufin jamโ€™in dalibai, kamar Musulman ne, abinda ke nufi jamโ€™in Musulmi, su Dalibai ne wadanda suka gogu a karatun zaure, kamar yadda yake a alโ€™adar Kasar su

(2) Mazhabarsu ta Aqeedah Maturidiyya ce ta Abu Mansur Almaturidi, daya ne daga cikin manyan Malaman Sunnah na zamaninsa, Mazhabarsa tana kusa sosai da Mazhabar Abul Hasanil Ashโ€™ari.
Yadda wasu suke munana zato a garesu, Taliban a gurin โ€˜yan Boko Haram da ISIS suna musu kallon โ€˜yan bidiโ€™ah ne wadanda jininsu ya halatta, saboda wai Taliban sun sabawa mazhabar Salafiyya wadanda suke binta

(3) Taliban Mazhabarsu ta Fiqhu Hanafiyya suke bi, don Mazahabarsa ce ta yadu a Kasashen su tun farkon zuwan Musulunci, kuma da ita suke shariโ€™ah, kamar dai mu nan Nigeria muke bin mazhabar Malikiyyah

(4) Taliban basu da dangantaka da wata kungiyar taโ€™addancin addini ko siyasa, balle kungiyoyi masu yawan kafirta Musulmi

(5) Amurka ta tuhumi Taliban da goyon bayan taโ€™addanci saboda kin mika musu Usama bin Laden don su hukuntashi a shekarar 2001, su kuwa Taliban sunyi aiki da ilmin da suka sani wanda ya haramta sallama Musulmi ga kafurai, har suka yarda da gushewar mulkinsu akan dabbaka Sunnar Manzon Allah (SAW)

(6) Taliban kwararru ne kuma gogaggu ne a iya mulkin jamaโ€™a, ba kamar yadda kafofin yada labaran turai ke bata su ba, ko da yake baโ€™a rasa su da wata kura-kurai wadanda ba wani โ€˜dan adam dake iya rabuwa da kuskure, amma alherinsu yafi kuskurensu yawa nesa ba kusa ba.
Kuma mulkinsu a Kasar Afghanistan yafi na Amurkawa masu yada addinin Kiristanci karfi da yaki, kamar yadda yafi na Iran da take kokarin shiga ta yayyaga Kasar, ta yada shiโ€™anci kamar yadda takeyi yanzu haka a Iraqi

(7) Wasu mutane na yi musu hukunci da nauโ€™in tufafinsu, ace wai suna tauye hakkin mata, suna yi musu kulle, wannan ba haka bane, irin tufafinsu na alโ€™ada suke sawa mazansu da matansu, ko zaman Amurka a Kasar na shekara 20 bai canza matansu daga yin lullubi da sanya niqabi ba

(8) Bayyanar kungiyoyi masu daโ€™awar jihadi na duniya irinsu Boko Haram, ISIS da sauransu ya sa wasu Musulmi ba su son jin maganar jihadi, abinda ke sa su jin tsoron Taliban, alhali Taliban ta banbanta da irin wadancan kungiyoyi masu yawan kafirta Musulmi.

Su Taliban mutane ne masu kokarin adalci hatta ga abokan gabar su, kuma kasancewar su jagorori a Kasar Afghanistan yafi alheri akan Amurka (Kafirai) ko Iran โ€˜yan shiโ€™ah

Allah Ka daukaka Musulunci da Musulmai a duk inda suke Amin

Harin ฦณan Bindiga Na ฦ˜ara Ta'azzara A ฦ˜asar Amurka

Mutane 10 Sun Mutu Sakamakon Harin ฦŠan Bindiga A Walmart Na ฦ˜asar Amurka ฦณan sanda sun ce wani ษ—an bindiga ya harbe mutane da da...